Allah ka shige mana gaba a wannan lokaci da muke – Ministan Buhari yayi addu’a a zaman majalisar zartarwa

Allah ka shige mana gaba a wannan lokaci da muke – Ministan Buhari yayi addu’a a zaman majalisar zartarwa

Ministan bayanai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed a ranar Laraba ya nemi zabin Allah ga gwamnati mai ci “a wannan lokaci da Najeriya ke ciki.”

Mohammed ya fadi hakan ne a yayinda yake addu’an bude taro a zaman majalizar zartarwa da ake yi a duk mako a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari wadda ya dawo daga Lome, kasar Togo, inda aka nada shi a matsayin shugaban kungiyar ECOWAS ne ya jagoranci zaman.

Allah ka shige mana gaba a wannan lokaci da muke – Ministan Buhari yayi addu’a a zaman majalisar zartarwa
Allah ka shige mana gaba a wannan lokaci da muke – Ministan Buhari yayi addu’a a zaman majalisar zartarwa

An fara zaman ne wadda ya samu halartan mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo karfe 11am da yan mintoci kadan.

KU KARANTA KUMA: Ba zan sauya sheka daga APC ba – Mataimakin kakakin majalisa

Jam’iyyar APC ta sake samun Karin wadanda suka barta a ranar Talata, inda shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, Gwamnan jihar Kwara, Abdulfatah Ahmed da jakadan Najeriya a kasar Afrika ta Kudu, Alhaji Ahmed Ibeto suka koma PDP.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel