Jerin Shugabannin Kasashen da su kayi shekara da shekaru su na mulki

Jerin Shugabannin Kasashen da su kayi shekara da shekaru su na mulki

A Afrika dai a kan samu shugabanni su dade su na mulki, wasu ma har ta kai su daura ‘Ya ‘yan su. Yanzu mun kawo maku jerin wadanda su ka fi kowane dadewa a kan karaga ganin cewa Paul Biya na neman zarcewa kan kujerar sa a Kamaru.

1. Shugaban Kasar Guinea

Shugaba Teodoro Obiang Nguema na Kasar Equatorial Guinea ya shafe shekara 39 yana mulkin Kasar sa. Teodoro Nguema ya hau mulki ne a shekarar 1979 lokacin yana Matashi. Yanzu yana wa’adin sa na 7.

Jerin Shugabannin Kasashen da su kayi shekara da shekaru su na mulki
Teodoro Obiang Nguema yayi shekaru aru yana mulki

KU KARANTA: Ashe cikin Kakannin Barack Obama akwai Musulmai?

2. Shugaban Kasar Kamaru

A halin yanzu bayan Teodoro Obiang Nguema babu Shugaban kasar da ya kai Paul Biya na Kasar Kamaru dadewa a kan mulki. Biya yayi shekara 35 yana mulkin Kasar Kamaru kuma yana sa ran zarcewa bana.

3. Shugaban Kasar Kongo

Denis Sassou Nguesso yayi shekaru 34 a kan karagar mulkin Kasar Kongo idan aka hada wa’adin da yayi. Da farko Sassou Nguesso yayi mulki a 1979 har zuwa 1992. Bayan an gama yaki a kasar kuma ya kara dawowa kujerar a a 1997.

Bayan nan kuma akwai irin su Shugaba Yoweri Museveni na Uganda wanda yayi shekaru 32 yana mulki. A Kasar Sudan ma kuwa Shugaba Omar Al-Bashir ya shafe shekara 29 yana kan karaga. A nan kusa Chad Idriss Deby ya hau mulki ne tun 1990.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel