Majalisa ta amince da naddin sabon mataimakin gwamnan jihar Bauchi

Majalisa ta amince da naddin sabon mataimakin gwamnan jihar Bauchi

A yau Juma'a ne majalisar Jihar Bauchi a tantance kana ta amince da Audu Katagum a matsayin sabon mataimakin gwamnan Jihar.

Majalisar ta amince da mataimakin gwamnan ne a zaman da tayi karkashin jagorancin kakakin majalisar Kawuwa Damina.

Majalisar ba ta bata lokacin wajen tantancewar ba don basu dauki sama da mintuna biyar ba wajen tantance Katagum.

Majalisar jihar Bauchi ta amince da sabon mataimakin gwamna a jihar
Majalisar jihar Bauchi ta amince da sabon mataimakin gwamna a jihar

KU KARANTA: Zargin rashawa: Gwamnatin tarayya ta sake gurfanar da wani Sanata a kotu

Dan majalisa mai wakiltan yankin Bura, Abdullahi Abdulkadir ya bukaci a amince da Katagum saboda dama ya yi aiki a matsayin shugaban ma'aikata a karkashin gwamnatin gwamna Mohammed Abubakar.

Ibrahim Katagum, dan majalisa mai wakiltan Katagum ne ya goyi bayan bukatar tantance shi cikin gagawa.

Daga bisani majalisar ta tabbatar dashi a matsayin mataimakin gwamnan jihar Bauchi.

A baya, Legit.ng ta kawo muku rahoto inda tsohon mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Injiniya Nuhu Gidado ya yi murabus daga mukaminsa a ranar 24 ga watan Mayu.

Gwamnan kuma a watan Yuni ya zabi shugaban ma'aikatansa, Katagum don maye gurbin Gidado da ya yi murabus a matsayin mataimakin gwamnan.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel