Takaitaccen Tarihin Sarkin Zazzau na 18 Shehu Idris

Takaitaccen Tarihin Sarkin Zazzau na 18 Shehu Idris

Jaridar Rariya ta tsakura takaitaccen tarihin Sarkin Zazzau Shehu Idris daga littafin nan na kasar zazzau a jiya da yau. Mun dauko kadan daga ciki domin kawo maku takaitaccen tarihin na Shehu Idris.

An haifi Sarkin Zazzau wanda shi ne na 18 a jeringiyar Daular Fulani da ke Sarautar Kasar Zazzau a shekarar 1936. Mahaifin sa shi ne Malam Idrisu Auta wanda ‘Da ne wurin Sarkin Zazzau da aka yi daga Kasar Katsina watau Malam Sambo.

Takaitaccen Tarihin Sarkin Zazzau na 18 Shehu Idris
Shehu Idris ya zama Sarkin Zazzau a shekarar 1975

Shehu Idris yayi karantu ne a Makarantar Firamare ta Kofar Kuyambana da ke cikin Birnin Zazzau inda ya kammala a 1950. Daga nan kuma ya wuce Midil yak are a 1955. Bayan Midil Mai martaba ya tafi Makarnatar koyan Malanta ta Katsina.

A 1957 ne Shehu Idris ya kare Makarntar koyon malanta ya kuma fara aiki na N-A a matsayin Malamin Makaranta. Shehu Idris ya koyar a Makarantu da dama a Garuruwan Kasar Zazzau. Daga baya ne dai Shehu Idris ya ajiye aikin Malanta.

KU KARANTA: Kano ta yi wa Karuwai zafi a cikin watan Azumi

Mai martaba yayi kwas a Makarantar koyon aiki da ke Jami’ar Ahmadu Bello a Kongo inda bayan ya kammala a 1961 ya fara aiki a ofishin Sarkin Zazzau Aminu a matsayin Sakataren fadar Sarki. Daga nan kuma ya shiga Gwamnatin Kasar Arewa.

A 1967 ne Shehu Idris ya je Kasar waje inda bayan yayi wani kwas aka ba shi Hakimin Birni da kuma sarautar Dan Madami a 1973. Bayan rasuwar Sarki Aminu ne a wannan lokaci Shehu ya zama Sarki na 18 a Kasar Zazzau kuma daga gidan Katsinawa.

Yanzu dai shekaran Mai Martaba Sarki 43 a kan karagar mulki. Mai martaba ya dare kujerar Sarauta ne a 1975 lokacin bai kai shekaru 40 a Duniya ba. Mai martaba Shehu Idris yana da mata 4 da ‘Ya ‘ya da dama.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel