Majalisar Malaman Musulunci sun yi Allah-wadai da aikin Gwamna El-Rufai
- Majalisar Malaman Kaduna sun yi Allah-kyauta da aikin Gwamnan Jihar
- Sheikh Usman Baban-Tine yace sam bai dace Gwamna ya rika tsinuwa ba
- Babban Malamin yake cewa tsinuwa idan ta fita ba ta faduwa kasa banza
Mun samu labari cewa Majalisar Malaman addinin Musulunci na Jihar Kaduna sun yi Allah-wadai da abin da Mai girma Gwamnan Jihar yayi na tsinewa wasu ‘Yan Majalisar Jihar albarka kwanakin baya.

Asali: Facebook
Kamar yadda labari ya zo mana Shugaban Majalisar Malaman Jihar Sheikh Usman Abubakar Baban-Tine yayi jawabi a gaban ‘Yan jarida a makon nan inda yace kalaman Gwamnan Jihar na kwanakin baya sam ba su dace ba kuma su na da hadari.
Usman Baban-Tine take cewa a matsayin su na Malamai masu fadar gaskiya dole su fito su yi tir da wannan danyan aiki na Gwamna Nasir El-Rufai. Babban Malamin yace bai dace tsinuwa ta rika fitowa daga bakin Shugabanni da ke mulki ba.
KU KARANTA: An nemi Kotu ta janye belin Sanatan Kogi Dino Melaye
Shehin Malamin yake cewa a maimakon a rika kokarin kawo abin da zai kawar da fitina sai kuma a rika jin Mai Girma Gwamna na neman tada-zaune tsaye domin manufar siyasa ba daidai bane. Sheikh Baban-tine yace tsinuwa ba ta fadi kasa banza.
Kwanaki dai Gwamnan na Kaduna ya tsinewa Sanatocin Jihar saboda sun hana a ba Jihar Kaduna damar cin bashi a bankin Duniya. Sai dai masu kare Gwamnan sun ce dama dai duk mutum ajizi ne kuma zai fi kyau a ba Gwamnan shawara a sirri.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng