Kananan hukumomi biyar da PDP ta bawa APC mamaki a zaben jihar Kaduna

Kananan hukumomi biyar da PDP ta bawa APC mamaki a zaben jihar Kaduna

A jiya litinin ne hukumar zaben jihar Kaduna (SIECOM) ta bayyana cewar ta sakamakon zaben karamar hukumar bai kammalu ba, kamar yadda kamfanin dillancin Najeriya (NAN) ya rawaito.

Baturen zabe a karaamar hukumar Chikun, Samuel Ndams, ya bayyana cewar sakamakon mazabu bakwai ne daga cikin mazabu 12 ya shigo hannun sa.

Mista Ndams y ace sakamakon mazabu biyar ya shigo hannun sa ba a wurin tattara sakamako ba amma bayan ya tuntubi shelkwatar SIECOM sai ta bayar da shawarar a bayyana sakamakon da cewar bai kammalu ba.

Kananan hukumomi biyar da PDP ta bawa APC mamaki a zaben jihar Kaduna
Gwamnan jihar Kaduna; Malam Nasir El-Rufa'i

Sakamakon da hukumar zaben ta fitar ya nuna cewar jam’iyyar APC ta lashe kananan hukumomi 12, yayin da jam’iyyar PDP ta lashe zabe a kananan hukumomi biyar, sannan an dakatar da sakamakon kananan hukumomi uku.

Kananan hukumomin da APC tayi nasara sune; Kubau, Giwa, Ikara, Lere, Sabon Gari, Igabi, Kaduna ta Arewa, Zaria, Soba, Makarfi, da Birnin Gwari.

DUBA WANNAN: An kama mabiya Shi'a 60 bayan raunata 'yan sanda biyu

PDP tayi nasara a kananan hukumomin; Jema’a, Zangon Kataf, Kachia, Sanga, da Kauru.

Kamfanin dillanci labarai y ace bai samu sakamakon kananan hukumomin Kagarko da Kajuru ba, yayin da ake cigaba da jiran sakamakon zaben karamar hukumar Kaduna ta kudu.

A yayin da jam’iyyar APC ta bayyana gamsuwar tad a sakamakon zaben kananan hukumomin, jam’iyyar PDP tayi korafin cewar an tafka magudi.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng