Kallabi tsakanin rawwuna: Wata daliba daga jihar Katsina ta ciri ruta a jami’ar Saudiyya

Kallabi tsakanin rawwuna: Wata daliba daga jihar Katsina ta ciri ruta a jami’ar Saudiyya

Wata daliba yar asalin jihar Katsina dake karatu a jami’ar koyon likitanci na Batterjee dake jidda a kasar Saudiyya ta zamto zakakura, gwana kuma wanda tafi dukkanin daliban kwalejin hazaka, inji rahoton Daily Trust.

Majiyar Legit.ng ta ruwaito dalibar mai suna Ummulkulthum Abubakar Sadiq ta samu digiri a karatun likitanci mai daraja ta daya, kamar yadda shuwagabannin kwalejin suka sanar a ranar yaye dalibanta.

KU KARANTA: Jana’izar Sheikh Isiyaka Rabiu: Gwamnatin jihar Kano ta sanar da ranar hutu

Jami’ar Batterjee ta karramar Likita Ummulkulthum da wata babbar kyauta a ranar bikin yaye dalibai da jami’ar ta shirya a ranar Asabar 5 ga watan Mayu, sakamakon hazakar da ta nuna a shekarun data kwashe tana koyon likitanci a jami’ar.

Kallabi tsakanin rawwuna: Wata daliba daga jihar Katsina ta ciri ruta a jami’ar Saudiyya
Ummulkulthum da mahaifinta

Tarihin Ummkulthum ya nuna ta halarci makarantar ABC Academy, da Nurul Bayan International Academy, inda ta kammala karatunta a kwalejin Nigeria Tulic International College a shekarar 2011.

Shi ma mahaifin Likitan, Sanata Abubakar Sadiq Yaradua, tsohon wakilin al’ummar jihar Katsina ta tsakiya a majalisar dattawa, ya bayyana cewa tun a shekarar 2005 yar tasa ta yi saukan Qur’ani mai girma, inda ta haddace shi a tsakanin shekarar 2014 zuwa 2018.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng