Kasar Saudiyya ta zartar hukuncin kisa kan matashin da ya yi ridda tare da yin batanci ga Annabi

Kasar Saudiyya ta zartar hukuncin kisa kan matashin da ya yi ridda tare da yin batanci ga Annabi

Kasar Saudiyya ta zartar da hukuncin kisa a kan wani mutum da ya yi ridda tare da yin kalaman batanci ga Annabi.

Hankalin hukuma ya kai kan Ahmad Al-Shamri a shekarar 2014 bayan ya saka wasu faifan bidiyo dake nuna akidar mulhidanci a dandalin sada zumunta. An gurfanar da shi gaban kotu bisa tuhumar sa da batanci da kuma mulhidanci tare da yanke masa hukuncin kisa a shekarar 2015.

Da farko matashin, Al-Shamri; mai shekaru 20, ya bayyana cewar yana cikin maye ne lokacin da ya aikata laifin da ake tuhumar sa da shi saidai uzurin shi bai samu shiga ba a gaban kotun.

Kasar Saudiyya ta zartar hukuncin kisa kan matashin da ya yi ridda tare da yin batanci ga Annabi
Kasar Saudiyya ta zartar hukuncin kisa kan matashin da ya yi ridda tare da yin batanci ga Annabi

Hukumomi a kasar Saudiyya sun yi dogaro da ayoyin Qur'ani wajen yanke wa Al-Shamri hukunci. Za kashe shi ta hanyar harbi ko datse masa kai.

DUBA WANNAN: Da dumin sa: Abubuwa biyar da Trump ya fada a kan Najeriya yayin ganawa da Buhari

Kungiyar kare hakkin bil'adama ta Amnesty ta saka kasar Saudiyya a matsayin kasa ta uku a jerin kasashe dake zartar da hukuncin kisa a kan mutane.

Ra'ayin masu amfani da dandalin sada zumunta ya rabu a kan wannan hukunci da aka zartar a kan Al-Shamri, inda wasu ke nuna cewar hukuncin ya yi tsauri yayin da wasu kuma ke murna.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel