Rundunar Sojin kasa ta damke wasu 'yan Kungiyar Asiri 23 da 15 masu Fashe Bututun mai a jihar Legas

Rundunar Sojin kasa ta damke wasu 'yan Kungiyar Asiri 23 da 15 masu Fashe Bututun mai a jihar Legas

A ranar Asabar din da ta gabata ne hukumar Sojin kasa ta Najeriya ta bayyana cewa, ta samu nasarar cafke wasu mutane 23 da ake zargin 'yan kungiyar asiri ne a yayin da sake gudanar horaswa gami da tantance sabbin masu shiga 'yan kungiyar.

Rundunar Sojin ta kuma bayyana cewa ta samu nasarar cafke wasu mutane 15 da ake zargin su da Fashe Bututun mai inda aka damke su tare da jarkoki 31 na tataccen man fetur.

Rundunar Sojin kasa ta damke wasu 'yan Kungiyar Asiri 23 da 15 masu Fashe Bututun mai a jihar Legas
Rundunar Sojin kasa ta damke wasu 'yan Kungiyar Asiri 23 da 15 masu Fashe Bututun mai a jihar Legas

Manjo Janar Enobong Udoh, Kwamandan dakarun sojin kasan dake bataliya mai lamba 174 a yankin Ikorodu na jihar Legas shine ya bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai.

KARANTA KUMA: Gwamnati ta tarwatsa wasu Gidajen sayar da Barasa da na Karuwai a jihar Jigawa

Udoh wanda Janar Moundhey Ali ya wakilta a yayin wannan sanarwa ya bayyana cewa, an yi nasarar cafke miyagun ne a lokuta daban-daban sakamakon leken asiri da kuma tattaro bayanai na sirri.

Legit.ng ta fahimci cewa, rundunar Sojin ta cafke masu kishi da zaman lafiya na kasar nan ne a yankunan jihar Legas tun a ranar 16 ga watan Afrilu da kuma wasu a sassa na jihar Ogun.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko buƙatar bamu labari, tuntuɓe mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://facebook.com/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel