Da duminsa: Wasu 'yan majalisar wakilai biyu sun sallama jam'iyyar PDP, sun canja sheka

Da duminsa: Wasu 'yan majalisar wakilai biyu sun sallama jam'iyyar PDP, sun canja sheka

Wasu 'yan majalisar wakilai guda biyu, a yau, sun bayyana ficewar su daga jam'iyyar PDP yayin zamar majalisar na yau.

A wasikun da 'yan majalisar wakilan suka aike kuma shugaban majalisar, Yakubu Dogara, ya karanta sun bayyana cewar sun canja sheka daga PDP zuwa jam'iyyar APGA.

'Yan majalisar biyu; Ben Nwakwo da Anayo Nnebe, sun bayyana cewar sun fita daga jam'iyyar ta PDP ne saboda rikicin shugabanci da jam'iyyar ke fama da shi a jihar su ta Anambra.

Da duminsa: Wasu 'yan majalisar wakilai biyu sun sallama jam'iyyar PDP, sun canja sheka
majalisar wakilai

Jaridar premium times ta taba wallafa rahoton cewar dan majalisa Ben Nwakwo ya marawa jam'iyyar APGA baya ne a zaben gwamna da aka yi a jihar a 2017.

Wannnan shine karo na farko da wani mamba a majalisar ta wakilai ya canja sheka zuwa jam'iyyar APGA tunda aka rantsar da majalisar bayan zaben 2015.

DUBA WANNAN: An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

Ya zuwa yanzu jam'iyyar PDP ta rasa mambobi 15 a majalisar wakilai daga 2015 zuwa yanzu.

Jam'iyyar APGA na da mambobi guda uku, hakan ya saka ta cikin jerin jam'iyyun Najeriya uku dake da wakilci a majalisar wakilai.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel