An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

- An tabbatar da mutuwar wasu matasa biyu a unguwanni daban-daban dake cikin garin Bauchi

- Matasan sun rasa rayukan su ne a unguwannin Jahun da titin Wanka a garin Bauchi sakamakon rikici a kan lika fostar zabe

- Mazauna titin Wanka sun ce an kashe wani matashi a kofar gidansu kuma tuni har an binne shi bisa tsarin addinin Islama

An tabbatar da mutuwar wasu matasa biyu a unguwanni daban-daban dake cikin garin Bauchi.

Matasan sun rasa rayukan su ne a unguwannin Jahun da titin Wanka a garin Bauchi sakamakon rikici a kan lika fostar zabe.

Mazauna titin Wanka sun ce an kashe wani matashi a kofar gidansu kuma tuni har an binne shi bisa tsarin addinin Islama.

An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka
An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

Wani shaidar gani da ido, Mohammed Adam, ya shaidawa jaridar Daily Post cewar an kashe matasan ne a kan rikicin lika fostar zabe ko kuma cire ta.

Kakakin hukumar 'yan sanda a jihar Bauchi, DSP Datti Kamal, ya tabbatar da afkuwar lamarin ga Daily Post.

DUBA WANNAN: Jirgin yakin hukumar soji MI-35M ya yi ruwan nakiyoyi a kan motocin 'yan Boko Haram

A cewar sa, "mun samu rahoton kisan wani matashi, Abdulhaxiz Yunusa, da wasu matasa da ba a san ko su waye ba suka aikata a kofar gidansa."

Ya kara da cewar hukumar 'yan sanda na gudanar da bincike domin gano wadanda keda hannu cikin kisan.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng