Tattalin arzikin Najeriya ya kama hanyar mikewa a Gwamnatin Buhari

Tattalin arzikin Najeriya ya kama hanyar mikewa a Gwamnatin Buhari

- Alkaluma sun nuna cewa tattalin arzikin Najeriya na kara habaka

- Kayan masarufi na rage tsada a Najeriya ba kamar a lokacin da ba

- Kudin kasar wajen Najeriya na kara yawa bayan tashin man fetur

Mun samu labari cewa alkaluma sun nuna cewa tattalin arzikin Najeriya zai habaka a shekarar bana. Hakan na zuwa ne bayan da Najeriya ta samu kan ta cikin radadin tattalin arziki kwanakin baya a Gwamnatin Shugaba Buhari.

Tattalin arzikin Najeriya ya kama hanyar mikewa a Gwamnatin Buhari
Abubuwa sun fara sauki a Gwamnatin Shugaban kasa Buhari

Alkaluman da ke yawo na tattalin arzikin kasar nan sun nuna cewa za a samu cigaba wajen harkar tattali da karuwar jimillar kudin Kasa watau GDP. Bayan haka kuma darajar kudin kasar zai karu a kasuwa duk a wannan shekarar da aka shiga ta 2018.

KU KARANTA: Marasa zuwa Makaranta sun ragu a Gwamnatin Shugaba Buhari

Tattalin arzikin kasar ya habaka ne ta fannin raguwar tsadar kaya da kuma samun saukin kasuwanci yanzu haka. Abubuwa dai sun fara mikewa ne a Gwamnatin Shugaba Buhari bayan da aka kawo shirin ERPG da zai farfado da tattalin arzikin kasar kwanaki.

Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa kayan masarufi na rage kudi a Najeriya, haka kuma kudin kasar waje na cigaba da karuwa yanzu a asusu. Har wa yau darajar Dalar Amurka na raguwa yayin da Gwamnati ke sakin kudi na aikace-aikace a fadin kasar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel