Mai gida na ya fi so na a kan Mahaifiyar sa don haka ya sake ni – Wata ta fadawa Alkali
- Wani mutumi yayi mamaki bayan da sahibar sa ta maka sa a Kotu
- Matar ta sa dai tace ya fifita ta a kan Uwar sa da ta kawo sa Duniya
- Tace ba ya iya taimakon Mahaifiyar sa don haka ta nemi saki a Kotu
Kwanan nan mu ka kuma samu wani labari a Kasar Saudiyya idan wata Budurwa ta nemi Kotu ta raba auren ta mijin ta bayan da ta gano Mijin ta ya cika kaunar ta fiye da har Mahaifiyar sa a Duniya.

Wannan Mata mai shekaru 29 ta gigita Mai gidan ta bayan ta nemi a raba auren su saboda Mijin ta ya fifita ta ta a kan Mahaifiyar sa. Tace duk abin da ta ke so yana yi mata amma yana wulakanta Uwar sa don haka tace ba ta kaunar irin wannan namiji.
KU KARANTA: Aikin Shaidan ne inji wani Mutumi bayan ya bar Surukar sa da ciki
Yanzu haka dai Jaridar Saudi Gazette ba ta bayyana sunayen wadannan mutane ba. Wannan Mata tace duk wanda bai iya taimakawa Uwar sa ba abokin zama bane kuma zai yi iya yaudarar Matar sa ta aure a koyaushe don haka ta dauki wannan mataki.
An yabawa wannan mata a Kotu inda ake shar’ar da cewa ya kamata mutum ya fi daraja uwar sa kan kowa a Duniya. Wannan mai gida dai yayi mamaki ace mai dakin sa za ta bar sa duk da irin abin da yayi mata ya kauracewa dangin sa saboda ita.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng