Dalilin da ya sa na fito a Barauniya – Hafsa Idris

Dalilin da ya sa na fito a Barauniya – Hafsa Idris

Shahararriyar Jarumar fina-finan Kannywood, ace ta shigo harkar fim da kafar dama, Hafsa Idris, ta ce ta dauki tsawon watanni shidda bitar rubutaccen labarin fim din “Barauniya” shi ya sa ta taka rawar gani sosai a fim din kamar yadda gogaggun barayi ke yi.

Hafsa, wacce ake wa lakabi da ‘Barauniya’ ta bayyana cewa ta soma fim ne domin ba ta son zaman banza. A cewarta harkar fim ya fi aikin gwamnati saboda tana samun abunda ma’aikacin gwamnati baya samu.

Sannan kuma jarumar ta bayyana cewa da harkar fim ne take hidimomin gabanta daman a iyayenta da yan’uwa.

Jarumar ta ce ta koyi darasi da dama daga fim din “Barauniya” wanda shi ne na farko da ta fara yi a kamfanin shirya fina-finai na Kannywood.

Dalilin da ya sa na fito a Barauniya – Hafsa Idris
Hafsa Idris ta bayyana dalilin da yasa ta taka rawar gani a fim din barauniya

Jarumar, wadda ta soma fim a watan Disambar 2016, dalilin yin fim din Barauniya ya sa masu hada fina-finai na yin ruguguwar sanya ta a fina-finansu saboda yadda ta kware a lokaci guda.

KU KARANTA KUMA: Jirgin Shugaban kasa Buhari na nan inda aka ajiye shi har gobeJirgin Shugaban kasa Buhari na nan inda aka ajiye shi har gobe

Ta ce ko wani wata tana yin fim uku zuwa hudu saboda “amincewar da furodusoshi” suka yi mata wajen taka rawar gani a manyan fina-finai.

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng