Assha! Wani mai sana'ar walda ya dirka wa wata matar aure ciki a Abuja

Assha! Wani mai sana'ar walda ya dirka wa wata matar aure ciki a Abuja

Wata kotu dake a garin Abuja babban birnin tarayya ta bayar da belin wani mai sana'ar walda wanda yake da suna Abubakar Sadiq akan kudi Naira 30,000 bayan da aka kama shi da laifi dumu-dumu na yi wa wata matar aure ciki.

Wannan al'amari dai ya auku ne a garin Abuja kuma mijin matar mai suna James olanga shine ya shigar da karar a kotun dake zaman nata a Abuja.

Assha! Wani mai sana'ar walda ya dirka wa wata matar aure ciki a Abuja
Assha! Wani mai sana'ar walda ya dirka wa wata matar aure ciki a Abuja

Legit.ng dai ta samu labarin cewa wanda ake zargin ya amasa laifin sa amma kuma sai ya shaidawa kotun cewa shi bai san tana da aure ba shi yasa.

Yace fadawa kotun cewa sun hadu ne a matsayin su na baligai in da suka fada kogin soyayya amma bai taba sani cewa wai tana da aure ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng