Shugaba Buhari ya aikawa 'yan Najeriya sakon barka da Sallah

Shugaba Buhari ya aikawa 'yan Najeriya sakon barka da Sallah

- A cikin sakon sallar shugaban kasa Buhari ya bukaci ‘yan Najeriya da su zauna lafiya da juna su yi watsi da duk wani furucin da zai jawo tashin hankali

- Buhari ya ce ‘yan Najeriya su gode ma Allah da ya sa suka ga karshen Ramadan lafiya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aikawa musulmai da kiristocin Najeriya sakon gaisuwa a yayin bikin sallah, inda ya yi kira ga dukkan 'yan Najeriya da su zauna lafiya da juna su yi watsi da duk wani furucin da zai jawo tashin hankali.

KU KARANTA KUMA: YANZU-YANZU: An ga wata a Adamawa, Sokoto da Katsina - Sarkin Musulmai, Abubakar Sa'ad

Sakon na rubuce ne kama haka:

"Ina mai godiya ga Allah da muka kammala wannan watan Azumi na Ramadan. Ina mika sakon gaisuwa ga dukkan musulman Nijeriya da 'yan uwanmu Kiristoci a yayin bikin sallah.

"Allah ya sa mu dore kan darrusan da muka dauka a cikin watan na Ramadan, kamar tausasawa, yawaita ibada da sauransu.

"Ina kara jan hankalin 'yan Nijeriya da su kauracewa duk wasu kalamai da za su jawo tashin hankali a kasar nan. Mu zauna lafiya mu hada kai wanda shine silar ci gaban kowace kasa.

"Barka da sallah"

Sanarwa daga maitamakwa shugaba Buhari kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu.

Ku same a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng