An kama masu kai wa daliban Najeriya hari a India

An kama masu kai wa daliban Najeriya hari a India

Jami’an ‘yan sandan India sun cafke mutane shida da ake zargi da hannu wajen kaddamar da farmaki kan daliban Najeriya da ke karatu a kasar, abin da masu rajin kare hakkin dan adam suka bayyana a matsayin laifin nuna kyama.

Wasu yan India suna dukan yar Najeriya
Wasu yan India suna dukan yar Najeriya

Legit.ng dai ta gano wasu hotuna da aka watsa a kafafen sada zumunta sun nuna yadda wasu matasan India ke amfani da sandina da kujerun karfe wajen dukan daliban Najeriya a Greater Noida.

Wani babban Jami’an ‘yan sandan kasar Sujata Singh ya shaida wa majiyar mu cewa, nan gaba za su sake kama wasu mutane hudu da ake zargi a wannan lamari da ya dauki hankulan ‘yan Najeriya.

KU KARANTA: Hukumar WAEC ta fallasa wani Sanata

Hukumomin Najeriya sun kira jakadan India a kasar don amsa tambayoyi a birnin Abuja kan wannan batu.

An dai kai wa ‘yan Najeriyar hari ne bayan mutuwar wani dan India sakamakon kwan-kwadon kwayoyi fiye da kima, amma mazauna yankin Greater Nida suka zargi ‘yan Najeriya da hannu a mutuwarsa.

Kazalika farmakin ya shafi sauran daliban nahiyar Afrika da ke karatu a kasar ta India, lamarin da ya sa jami’an tsaro ke yi musu rakiya zuwa makarantu da shaguna don kare lafiyarsu.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Ga kuma wata uwa nan tana kuka an tafi mata da yaya

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng