Wasu yan mata guda 2 daga kabilar Igbo sun musulunta

Wasu yan mata guda 2 daga kabilar Igbo sun musulunta

Wasu matasan yan mata guda biyu yan kabilar Igbo daga Mbaise dake jihar Imo sun shiga addinin mususlunci.

Yan matan wadanda suka canja sunayensu zuwa na musulmai wato Zainab da Halimah sun kammala karatu daga makarantar Darus-salam.

Wasu yan mata guda 2 daga kabilar Igbo sun musulunta
Wasu yan mata guda 2 daga kabilar Igbo sun musulunta

A cewar shafin Facebook din Islamic Calling Family yan matan sun kammala karatunsu a jiya Laraba, 15 ga watan Maris.

KU KARANTA KUMA: Dalibar makaranta ta rasa idonta bayan harin da malami ya kai mata, amma kwararru sunce naira miliyan 1 zai iya dawo da ganinta

Islamic Calling Family ta rubuta a shafin ta na Facebook: “Wannan aikin Islamic Calling Family ne...

“Zainab da Halimah daga Mbaise sun kammala karatu daga makarantar Darus-salam jihar Kaduna a yau 15 ga watan Maris 2017. Alhamdulillahi yanzu suna da ilimin addini.”

Wasu yan mata guda 2 daga kabilar Igbo sun musulunta

Kalli bidiyo a kasa:

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng