Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno

Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno

- Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno wacce Boko Haram suka tarwatsa a shekarar 2015

- A shakarar 2015 Kungiyar Amnesty International ta zargi Boko Haram da kisan kiyashi a garin wanda ya ja hankalin duniya, amma rundunar sojin Najeriya ta musanta

Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno
Wasu daga cikin mazauna garin na gudanar harkar kasuwancinsu

Rahotanni na nuna cewa komai ya daidaita a garin Baga da ke jihar Borno.

A wasu jerin hotuna da wani mazaunin garin mai suna Baba Bala Meleh ya dauka, kuma Jaridar Rariya ta wallafa a dandalin sada zumunta da muhawara na Facebook a ranar 11 ga watan Janairu shekara 2017, hotunan sun nuna yadda jama’a ke hada-hadarsu ta yau da kullum a garin.

Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno
An zargi Boko Harm da kisan kiyashi a Baga a shekarar 2015

Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno
Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno

Garin na Baga na daya daga cikin garuruwan da Boko Haram ta mamaye ta kuma tarwatsa jama’ar garin tare da tilasta musu gudun hijira.

Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno
Al’amura sun daidaita a garin Baga ta jihar Borno

A wani rahoto da kungiyar Amnesty International ta fitar a shekarar 2015, ta ce Boko Haram ta yi barnar da ba a taba ganinta ba a tarihin fadace-fadacen ‘yan ta da kayar baya, a inda Boko Haram a lokaci guda ta hallaka mutane 2,000.

Sai dai a wani martani da rundunar sojin Najeriya ta bayar tdangane da rahoton, mai magana da yawon shalkwatar tsaro ta waccen lokacin, Manjo Janar Olukolade ya musanta rahoton tare da cewa mutanen da suka hallaka 150 ne, ciki har da ‘yan ta’addan.

Sai dai wasu majoyoyi na cewa, ‘yan Boko Haram a waccan lokacin sun ragargaza akalla garuruwa 16 na jihar a wasu jerin hare-hare da Boko Haram ta kai mutane 2,000 suka mutu ciki har da wadanda suka hallaka a tafkin Chadi a kokarinsu na tsira da rayukansu.

Ku cigaba da bin mu a shafin mu na Facebook a https://www.facebook.com/naijcomhausa/ da kuma a Tuwita a https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng