'Yan Najeriya na fadin ra'ayinsu kan jawabin A'isha Buhari

'Yan Najeriya na fadin ra'ayinsu kan jawabin A'isha Buhari

-Hajiya Aisha Buhari ta fasa kwai da kuma tayi magana akan hayaniyan da ke faruwa cikin jam’iyyar APC.

'Yan Najeriya na fadin ra'ayinsu kan jawabin A'isha Buhari

Uwargidan shugaban Najeriya, uwargida A'isha Buhari tace mutane sun fara kawo baraka cikin All Progressive Congress (APC)

A wata hira da gidan radiyon BBC sashen Hausa wand aka dan tsakuro ma jama'a ranar Talata 11 ga Oktoba, tace maigidanta bai san mafi yawan mutanen da ya nada cikin gwamnatinsa ba. 'Yan Najeriya na Tofa albarkacin bakinsu inda wasu ke cewa jawabin A'isha Buhari sheda ce akwai matsala cikin gwamnatin Buhari. Wasu kuma suna cewa wannan ba wani  na fadin abinda ta fada a bayan fage.

KU KARANTA:Rashin motar asibiti ya sanya wasu iyaye sun dauki gawar ‘yarsu a kurar ruwa

Da aka tambaye ta ko maigidanta ya san mutanen da ke tsakkiyar cece-kucen da ake ciki, tace: "Ko ya sani, ko bai Sani ba, wadanda suka zabe shi sun sani. Yana iya gani, kuma idan ka tambaye shi cikin mutane 50 da ya zaba, bai san 45 daga cikinsu. Ni ma ban sansu ba cikin shekaru 25 da nayi tare dashi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng