Jihar Zamfara
Rahotanni da muke samu sun tabbatar da cewa gungun yan bindiga karkashin Ado Aliero aun kashe Hakimin Dogon Dawa a garin Keta, Tsafe a jihar Zamfara.
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kewaye wani masallaci a jihar Zamfara sun sace masallata 40 ana tsaka da sallar Asuba. Sun tafi da masallata dajin Tsafe.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hari wani kauyen jihar Zamfara. 'Yan bindigan sun tattara mata da kananan yara zuwa daji yayin harin da su ka kai.
Rahotanni sun tabbatar da cewa Rundunar sojoji ta kama wata mata mai suna Fatima Isah Ile a Kanoma, bisa zargin taimakawa ‘yan ta’adda wajen ayyukansu.
Gamayyar kungiyar ma'aikatan jinya ta fara yajin aiki a jihar Zamfara. Sun yi gargadin cewa ba za su amince da wariyar da ma'aikatar lafiya ta jihar ke nuna musu ba.
Dakarun sojoji sun yi artabu da 'yan bindiga a jihar Zamfara. A yayin artabun an kashe 'yan bindiga masu yawa yayin da aka samu asarar rayukan wasu sojoji.
Wasu 'yan ta'adda dauke da makamai sun yi basaja wajen satar mutane a jihar Zamfara. Miyagun sun zo da sabon salo yayim da suka sace bayin Allah zuwa cikin daji.
An kama mutane 6 cikin wandanda ake zargi da kai hari wani masallaci ana sallar asuba a jihar Zamfara. Maharan sun tafi da wasu masallata yayin harin.
Mazauna Arewacin Zamfara sun nuna damuwa kan daukewar sabis na sadarwa a kananan hukumominsu, sun roki hukumar NCC ta shiga tsakani don dawo da sabis.
Jihar Zamfara
Samu kari