Amurka
Harin Amurka da Isra'ila a makaranta a Iran ya ja hankalin Majalisar Dinkin Duniya inda ta ce za ta gudanar da muhawara ta gaggawa kan harin da aka kai.
A labarin nan, za a ji cewa wasu daga cikin Amurkawa sun yi adawa da yadda ake kara tsawaita yaki da Iran bayan Shugaban Donald Trump ya haɗa kai da Isra'ila.
Kasar Iran ta gargadi Amurka kan tura karin sojoji Gabas ta Tsakiya, tana cewa tana sa ido sosai kan dukkan motsin rundunar yayin da ake ci gaba da yaki.
Fafaroma Leo ya yi kira ga shugabannin kowane banngare da ke yaki a Gabas ta Tsakiya su tsagaita wuta. Ya yi magana ne bayan shiga mako na 3 da yakin Iran da Amurka.
Kungiyar Hezbollah da ke marawa Iran baya ta kai farmaki kan jirgin Isra'ila yayin da ya yi yunkurin kai farmaki a kasar Lebanon. Isra'ila bata ce komai ba.
Gobara ta tashi a wani tsohon ginin da ke dauke da kotu da wasu ofisoshi n gwamnati a Amurka. Hukumomi sun sanar da cewa an dage zaman kotu zuwa wani lokaci.
Rundunar dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC), ta kaddamar da sababbin hare-hare kan Isra'ila. IRGC ta bayyana wuraren da ta farmaka.
Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa Amurka na tattaunawa da Iran kan wani tsari mai maki 15 domin kawo karshen yaki da kuma batun makamin nukiliya.
Kasashen Pakistan, Egypt da Turkey sun bayyana cewa za su jagoranci zaman sulhu tsakanin Iran da Amurka domin kawo karshen yakin da ake a Gabas ta Tsakiya.
Amurka
Samu kari