Kudu maso gabashin Najeriya
Zababben gwamnan Edo, Monday Okpebholo, ya nada Fred Itua a matsayin Babban Sakataren Yada Labarai don inganta sadarwa tsakanin gwamnati da al’umma.
Gwamnatin jihar Imo tana zargin tsohon kwamishina, Fabian Ihekweme da neman kudi daga Gwamna Hope Uzodinma da abokansa domin ya bar caccakarsa da yake yi.
Bayan yada rade-radin mutuwar Sanata Rochas Okorocha, Hadimin tsohon gwamnan jihar Imo ya yi martani kan labarin inda ya ce karya ce tsagwaronta.
Wata motar haya da ta kuccewa direba ta daki bakin gada, ta faɗa kogi a karamar hukumar Njaba da ke jihar Imo, duka fasinjojin cikin motar sun kwanta dama.
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Imo ta tabbatar da fashewar bom a kasuwar Orlu ta ƙasa da ƙasa da ke jihar Imo, ta ce miyagu 2 da suka dasa shi sun mutu.
Allah ya yi wa babban alkalin Ekiti, Mai shari'a Oyewole Adeyeye rasuwa bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya. An ce gini ya rufta kan alkalin shekarar baya.
Gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta ya nemi alfarmar malaman addini wurin taya shi da addu'o'i a gwamnatinsa inda ya fadi irin gudunmawar da suke bayarwa.
Wasu miyagu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun je har gona sun kashe manomi da ƴaƴansa guda biyu a yankin karamar hukumar Ivo ta jihar Ebonyi.
Gwamnan jihar Abia, Alex Otti ya sallami shugaban jami'ar ABSU da ke garin Uturu tare da mataimakansa daga aiki, ya naɗa waɗanda za su maye gurbinsu.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari