Kudu maso gabashin Najeriya
Wasu yan bindiga da ake kyautata zaton ƴan IPOB ne masu tilasta dokar zaman gida sun kashe dakarun rundunar AVS huɗu a jihar Anambra ranar Litinin
Tsohon kwamishina a jihar Ebonyi, Abia Onyike ya tattara kayansa daga jam'iyyar PDP zuwa APC mai mulki inda ya yabawa salon mukin Gwamna Francis Nwifuru.
Tsohon Ministan wasanni da matasa, Solomon Dalung ya koka kan garambawul a gwamnatin Bola Tinubu inda ya ce ya kamata a sallami 70% na Ministoci.
Hukumar NiMet ta yi hasashen cewa za a fuskanci hazo da ruwan sama a wasu jihohin Najeriya daga ranar Litinin, 11 zuwa Laraba 13 ga watan Nuwamba.
Zababben gwamnan Edo, Monday Okpebholo, ya nada Fred Itua a matsayin Babban Sakataren Yada Labarai don inganta sadarwa tsakanin gwamnati da al’umma.
Gwamnatin jihar Imo tana zargin tsohon kwamishina, Fabian Ihekweme da neman kudi daga Gwamna Hope Uzodinma da abokansa domin ya bar caccakarsa da yake yi.
Bayan yada rade-radin mutuwar Sanata Rochas Okorocha, Hadimin tsohon gwamnan jihar Imo ya yi martani kan labarin inda ya ce karya ce tsagwaronta.
Wata motar haya da ta kuccewa direba ta daki bakin gada, ta faɗa kogi a karamar hukumar Njaba da ke jihar Imo, duka fasinjojin cikin motar sun kwanta dama.
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Imo ta tabbatar da fashewar bom a kasuwar Orlu ta ƙasa da ƙasa da ke jihar Imo, ta ce miyagu 2 da suka dasa shi sun mutu.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari