Siyasar Najeriya
Wani kusa a jam'iyyar APC ta jihar Kano, Jadda Garko, ya yi zargin cewa an shirya masa zagon kasa don ka da ya samu mukami a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
A labarin nan, za a ji cewa Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya katse hutunsa a kasashen waje yayin da ake shirin mayar da Siminalayi Fubara kan kujerarsa.
Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta dura kan tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar bayan ya soki mulkin shugabam kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Dattawan jam'iyyar APC a jihar Ondo sun yi alkawarin samawa shugaba Bola Tinubu kuri'a miliyan 1.5 a 2027, sama da wanda Rabiu Kwankwaso ya samu a Kano.
Majalisar Dinkin Duniya ta gargadi jam'iyyun siyasa a Najeriya da su gujewa amfani da kalaman kiyayya, cin mutuncin juna da kage yayim shirin zaben 2027 mai zuwa.
Babban kusa a jam'iyyar NNPP, Buba Galadima, ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na kokarin tarwatsa 'yan adawa. Ya ce ba za ta yi sahihin zabe ba.
Tsohon mataimakin shugaban kasan Najeriya, Atiku Abubakar, ya yi kalaman suka kan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu. Atiku ya ce gwamnatin ta gaza sosai.
Babban kusa a jam'iyyar PDP, Segun Sowunmi, ya bayyana cewa zaben shekarar 2027, zai kasance ne a tsakanin jam'iyyun APC da PDP. Ya ce ba a batun ADC.
Sakataren jam'iyyar ADC na kasa, Rauf Aregbesola, ya bayyana cewa sun shirya kawo sabon tsari a fagen siyasar Najeriya. Ya nuna cewa akwai abubuwan da za a sauya.
Siyasar Najeriya
Samu kari