Haduran mota a Najeriya
An tabbatar da cewa jami'ar a hukumar LASRRA, Hajiya Serifat Olubukola Talabi, ta rasu kwana hudu kafin ritayarta da kuma zagayowar ranar haihuwarta.
Rahotanni daga jihar Ogun sun bayyana cewa wata tanka da ta dauko man fetur ta fashe a kan totin Abeokuta zuwa Sagamu, ana fargabar mutane da dama sun mutu.
Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar mutane 26 a hatsarin jirgin ruwan da ya rutsa da yan kasuwa ranar Litinin, Gwamna Ahmed Ododo ya yi ta'aziyya.
Rahotannin da muke samu sun tabbatar da cewa matashin malami, Isma’il Maiduguri daga jihar Borno, ya tsira daga mummunan hatsarin mota a hanyar Maiduguri.
'Yan sanda sun samu raunuka daban-daban yayin da hatsarin mota ya rutsada ayarin shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Rt Hon. Haruna Aliyu Dangyatin.
Yan uwan juna sun rasa rayukansu a wani mummunan hatsari da ya rutsa ayarin mataimakin kakakin Majalisar dokokin jihar Abia a hanyar dawowa daga Fatakwal.
Mai fafutukar kare hakkin dan Adam, Martins Vincent Otse da aka fi sani da VDM ya jagoranci hana motocin Dangote wucewa da rana a jihar Edo saboda jawo hadura.
A labarin nan, za a ji yadda wasu bayin Allah guda 12 su ka rasa rayukansu a wani mummunan hadari da ya hada da babbar mota a Garun Mallam da ke Kano.
Wasu ma'aurata, Abdulsalam da Zainab da mutane 3 sun rasa rayukansu sakamakon mummunan hatsarin motar da ya rutsa da su a titin Kurfi zuwa Katsina.
Haduran mota a Najeriya
Samu kari