Jihar Osun
Wasu al'ummar yankin Ipetumodu a jihar Osun sun shiga damuwa kan rashin sanin halin da sarkinsu, Oba Joseph Olugbenga Oloyede ke ciki tsawon lokaci.
Tsohon gwamnan Oyo, Rashidi Ladoja, ya musanta zargin da jigon APC, Bisi Akande ya yi cewa yana da hannu a kisan tsohon minista a Najeriya, Bola Ige.
Rikici ya barke a garin Esa-Oke bayan nadin sabon sarki, inda wasu suka kai farmaki da kashe mutane da dama. ‘Yan sanda sun ce ana kokarin shawo kan lamarin.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hari wani kauye a jihar Osun yayin da ake rigimar sarauta. Sun harbi mutane da dama tare 'yan sanda bakwai.
Aregbesola ya yafe wa Olaboye da ya nemi gafara kan yunƙurin kashe shi a 2006. Yayin da ya yiwa mutumin nasiha, tsohon gwamnan ya ce bai rike shi a zuciya ba..
Dan majalisar wakilai karkashin jam'iyyar PDP a Osun, Oluwole Oke, ya ce tsohon gwamna, Ogbeni Rauf Aregbesola har yanzu yana da tasiri a siyasar jihar.
Gwamnatin Osun ta ce ta shirya daukaka kara bayan hukuncin kotu, inda ta bukaci a zauna lafiya har sai kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan rigimar sarauta.
Jam'iyyar APC ta nesanta ministan harkokin tattalin arzikin ruwa, Gboyega Oyetola daga neman takarar gwamnan jihar Osun. APC ta ce 'yan adawa ke yada fastocin karya.
Jam'iyyar APC ta dauki matakin kora kan tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola daga jam'iyyar. APC ta kori tsohon gwamnan ne bisa zargin cin amana.
Jihar Osun
Samu kari