Jihar Osun
Jam'iyyar PDP ta shiga jimami bayan rasuwar dan takararta na kansila a jihar Osun. Dan takarar na kansila ya rasu bayan ya yi fama da wata 'yar gajeruwar jinya.
Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya karyata raɗe-raɗin da ake yi cewa yana yunkurin komawa jam'iyyar APC, ya ce yana nan daram a jam'iyyar PDP.
Wani basarake a jihar Osun, Oba Jelili Olaiya ya bayyana cewa gaban 'yan sanda 'yan daba suka masa jina jina tare da matarsa da wasu 'yan fadarsa kan limanci.
Rundunar yan sanda ta ceto rayuwar wani basarake a jihar Osun bayan matasa sun lakada masa duka kan nada sabon limamin Juma'a da ya jagoranci sallah.
Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya ce ikirarin da APC ta yi cewa ya ciyo bashin kusan Naira biliyan 100 a asirce karya ce da ba ta da tushe ballantana makama.
Duk da korafe-korafe da ake yi kan kafa kotunan Shari'ar Musulunci, an yada idiyon Sheikh Dawood Malaasan da ya jawo cece-kuce a jihohin Yarbawa.
Tsohon mataimakin gwamnan jihar Osun, Clement Adesuyi Haastrup ya zama sabon sarki a masarautar Ijesa a matsayin Owa-Obokun bayan kada kuri'a kan nadin.
Gwamna Adeleke ya yi afuwa ga dan shekara 17 da kotu ta yankewa hukuncin kisa tare da wasu mutum 52, yana mai nuna jin kai da yafe wa wadanda suka tuba.
Tsohon Ministan lafiya a Najeriya, Farfesa Stephen Debo Adeyemi ya shiga takarar neman sarautar Owa Obokun na Ijesa da ke jihar Osun bayan mutuwar sarki.
Jihar Osun
Samu kari