Jihar Niger
Kamar yadda kididdiga ta nuna, jihohin Katsina, Sokoto, Kano, Jigawa, Kebbi, Neja da Yobe sun fitar da sama da N28.3b domin ciyar da al'ummarsu abinci a Ramadan.
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaro Bago, ya bada hutun kwanaki biyar a jihar domin raba kayan tallafi a fadin jihar. Hutun zai fara mako mai zuwa.
Bayan janye tallafin man fetur wanda ya haifar da tsadar rayuwa a Najeriya, akwai gwamnonin jihohi 12 da suka yi karin albashi. Legas da Ondo na biyan N35,000.
Gwamnan jihar Neja, Muhammad Umar Bago, ya amince da ƙarin N20,000 a albashin ma'aikatan jiharsa, ya kuma ba da umarnin a fara tura masu nan take.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci gwamnonin jihohin kasar nan da su samar da filayen kiwo ga makiyaya don kawo karshen rikicinsu da manoma.
An yi kazamin karo tsakanin mutanen kauyen Tswako Makun da na Gbangba Dzuko, a karamar hukumar Gbako ta jihar Neja. Lamarin ya yi sanadiyar rasa rayuka da dukiyoyi.
Gwamnatin jihar Neja ta sanar da cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai kaddamar da tashar jirgin saman Minna wacce aka sanya wa sunansa a ranar Litinin.
Allah ya yi wa Alhaji Muhammad Egba Enagi rasuwa, m5arigayin shi ne mahaifin matar gwamnan jihar Neja, Fatima Bago wanda ya riga mu gidan gaskiya da shekaru 90.
Yan sanda sun yi nasarar kama mutum 25 da ake zargi da aika muggan laifukan ƴan bindiga a jihar Neja, kwamishinam ƴan sanda ya ce sun fara bada bayanai.
Jihar Niger
Samu kari