Masu Garkuwa Da Mutane
Rahotanni sun nuna cewa wasu hatsabiban 'yan bindiga sun sace sace mai martaba Ojibara na Bayagan, watau Oba Kamilu Salami, a safiyar ranar Asabar din nan.
Wasu ma'aurata da suka fada hannun maau garkuwa da mutane a jihar Edo sun roki yan Najeriya su taimaka su hada masu kudin fansa Naira miliyan 50.
Kungiyar Diocese ɗin Katolika ta Kontagora ta fitar da sunayen mutum 265 — malamai, ma’aikata, daliban sakandare da firamare — da har yanzu suke hannun ’yan bindiga.
Mai magana da yawun majalisar dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya bayyana cewa Majalisa ta aminta cewa gwamnati ba ta biya kudin fansar daliban Kebbi ba.
'Yan bindiga dauke da miyagun makamai sun bude wuta kan mai uwa da wabi a Abuja, inda suka yi garkuwa da mata shida da kuma wani yaro dan shekara 16.
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari makarantar sakandare ta Kiri a Kogi, inda suka kashe mutum biyu, amma gwamnati ta tabbatar cewa ba a sace ɗalibi ko guda ɗaya ba.
Rundunar ’yan sandan Kwara ta tabbatar da sace mutane 10 a Isapa, tare da kaddamar da aikin ceto bayan harin da ake zargin makiyaya ne suka kai garin.
’Yan bindiga sun kai hari a Biresawa da wasu kauyuka a Tsanyawa, Kano, suka sace akalla mutum 8, ciki har da mata da matafiya. Mazauna sun tsere cikin dare.
Sojojin Najeriya sun kama wani babban mai garkuwa da mutane, Abubakar Bawa, a Wukari, yayin Operation Zafin Wuta da ke dakile aikace-aikacen miyagu a Taraba.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari