
Manyan Labarai A Yau







Shugaban kamfanin MTN na farko kuma attajirin ɗan kasuwa da ya kafa bankin Diamond, Pascal Gabriel Dozie ya kwanta dama, mun haɗa maku abubuwan sani gane da shi.

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya tuna da ma'aikatan da suka yi ritaya da wadanda suka rasu. Gwamnan ya umarci a fitar da kudade domin biyansu hakkokinsu.

Naira ta fadi zuwa N1,629/$ a kasuwar NFEM duk da tallafin CBN. Bukatar dala daga 'yan kasuwa da masu zuba jari na ci gaba da haifar da matsin lamba ga Naira.

Hatsarin mota ya yi ajalin wasu fitattun mawaƙan ikilisiyya su 4 a jihar Ogun, hukumar kiyaye haɗurra watau FRSC ta bayyana cewa hatsarin ya auku ne sabida gudu.

Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Katsina. 'Yan bindigan sun hallaka mutane hudu tare da yin awon gaba da wasu da dama.

Ministan harkokin matasa na kasa, Kwamared Ayodele Olawande ya ce rashin lokaci ke hana shi shiga zanga-zang, ya gargaɗi matasa su guji barnata kayan gwamnati.

Mai magana da yawun shugaban hukumar zaɓe watau INEC ya buƙaci ƴan Najeriya su yi watsi da jita-jitar da ke nuna cewa shugaba Tinubu ya tsige Mahmud Yakubu.

CRACON ta roki Shugaba Tinubu ya kafa kwamitin bincike kan Ministan Tsaro, Badaru, bisa zargin cin hanci da sabawa doka ta hanyar gudanar da kasuwanci na sirri.

'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a karamar hukumar Kankia ta jihar Katsina. 'Yan bindigan sun hallaka mutane tare da raunata wasu daban.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari