Manyan Labarai A Yau
Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane akalla 12 a kauyen Lajinge da ke Sokoto, inda suka kona mutum shida da ransu tare da sace wasu mazauna kauyen.
Hukumar kula da gyaran manyan tituna ta kasa, FERMA, ta fara gyaran titin Kano Eastern Bypass mai tsawon kilomita 13 domin rage cunkoso da inganta zirga-zirga.
Gobara mai saurin bazuwa ta kusanci birnin Spokane da ke jihar Washington, lamarin da ya tilasta kwashe dubban mazauna yankin yayin da aka ayyana dokar ta baci.
Rahotanni sun ce ‘yan bindiga sun kashe sojoji shida tare da sace fiye da mutum 70 bayan sun kai hari Kasuwar Daji a karamar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara.
Iran ta musanta ikirarin Donald Trump cewa ta bukaci Amurka ta dakatar da sabbin hare-hare, tana mai cewa mashigin Hormuz zai ci gaba da kasancewa a rufe.
Amurka ta yi Allah-wadai da harin da ya kashe mutane akalla 30 a Kaduna, tana mai kira ga gwamnatin tarayyar Najeriya ta dauki mataki kan matsalar tsaro.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce rabon filaye ga jama'a zai rage matsalar gidaje, samar da arziki tare da inganta makomar iyalai a jihar.
Wani babban malami a Sashen Shari’a na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Dakta Umar Sani Bebeji, ya rasu bayan wani mummunan hatsarin mota da ya ritsa da shi.
Shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da harin da aka shirya kai wa Iran, yana mai cewa an cimma matsaya kan yarjejeniya da za ta iya bude mashigin Hormuz.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari