Labarin Sojojin Najeriya
Sojojin Najeriya sun kama hatsabibin shugaban 'yan bindiga Bako Wurgi, wanda ke da alhakin kisan sarkin Gobir, yayin da yake jinya a asibitin Shinkafi.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasara kan miyagun 'yan bindiga a jihar Taraba. Sojojin sun kuma yi nasarar kubutar da wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su.
Dakarun sojojin Najeriya sun ci gaba da bude wuta kan 'yan ta'addan Lakurawa. Sojojin sun lalata sansanonin 'yan ta'addan da ke a jihohin Kebbi da Sokoto.
Hedkwatar tsaro ta kasa (DHQ) ta sanar da nasarorin da dakarun sojoji suka samu a cikin makon da ya gabata. Sojojin sun kuma ceto mutanen da aka sace.
Dakarun sojojin Najeriya tare da hadin gwiwar 'yan banga sun yi arangama da 'yan ta'adda a jihar Zamfara. Sojojin sun hallaka 'yan ta'adda tare da kwato makamai.
Hafsun tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya ce 'yan ta'addar Boko Haram 129,417 ne suka mika wuya a watanni shida a Najeriya, daga Yuni zuwa Disamba.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu 'yan bindiga kwanton bauna a jihar Kaduna. Sojojin sun kuma kwato shanun da aka sace a rugar Fulani.
Sojojin Najeriya sun cafke rikakken dan bindiga mai garkuwa da mutane da yake raba makamai a jihohin Filato, Kaduna da Zamfara a yankin Bassa na Filato.
Dangin Bello Bodejo sun yi kira ga sojoji da su gaggauta sako shi tare da ba da dama ga lauyoyi su gan shi, suna neman adalci kan lamarin Tudun Wada.
Labarin Sojojin Najeriya
Samu kari