
Zaben jihohi







Yayin da ake shirin gudanar da zaben gwamna a jihar Anambra, jam'iyyar PDP ta rufe siyar da fom ɗin takara amma ba wanda ya siya ko nuna sha'awa.

Gwamnatin jihar Kaduna ta gargadi tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufa'i a kan ya daina tsoma masu baki a cikin a yanayin gudanar da mulkin gwamna Uba Sani.

Shugaban APC na Kano, Abdullahi Abbas ya bayyana yi martani ga karamin Ministan gidaje da raya karkara, Yusuf Abdullahi Ata kan komawarsa kujerar shugaban jam'iyya.

Jam'iyyar LP na ci gaba da rasa jiga-jiganta ga APC da PDP, ciki har da Valentine Ozigbo, dan takarar gwamna, wanda ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar a Anambra.

Valentine Ozigbo ya koma APC daga LP, yana neman takarar gwamna a Anambra. Bashir Ahmad ya ce jam’iyyun adawa za su rushe kafin nan da babban zaben 2027.

PDP ta fara sayar da fom ɗin takarar gwamnan Anambra, zaɓen fidda gwani zai gudana 5 ga Afrilu, yayin da za a mika sunan ɗan takara zuwa ga INEC a ranar 22 ga Mayu.

Majalisar wakilai ta saurari bukatar kirkirar sababbin jihohi uku: Oke-Ogun, Ijebu da Ife-Ijesa daga Hon. Oluwole Oke. Majalisar ta tattauna kan muhimman kudurori.

Hukumar zabe ta kasa (INEC) ta kalubalanci tsohon kwamishinan zaben jihar Adamawa, Hudu Ari ya kare kansa a gaban kotu kan zarge-zargen da ya gabatar.

Kungiyar kwadago ta Najeriya watau NLC ta nuna damuwa kan yadda gwannoni ke barin jihohinsu su tafi Abuja duk da halin ƙuncin rayuwar da jama'arsu ke ciki.
Zaben jihohi
Samu kari