Labaran garkuwa da mutane
'Yan bindiga sun kai farmaki garin Kahutu da ke ƙaramar hukumar Ɗanja a jihar Katsina, sun yi awon gaba da mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara.
Yan bindigan da suka yi garkuwa da limamin coci, Mikah Suleiman sun ɗauki bidiyonsa yana neman agajin mutane, ya ce rayuwarsa na cikin haɗari a wurin ƴan fashi.
Rundunar ƴan sanda ta tabbatar da cewa ta samu rahoton sace wata mata mai tsohon ciki yayin da take hanyar zuwa asibiti a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.
Dakarun rundunar sojojin Najeriya sun yi nasarar ƙara rage mugayen iri a sassa daban-daban na ƙasar nan cikin mako 1, sun ceto ɗaruruwan mutanen da aka sace.
Masu garkuwa da mutane ɗauke da manyan bindigu sun tafi da Madakin Shabu jim kaɗan bayan ya fito daga Masallaci lokacin Sallar Isha'i a jihar Nasarawa.
Sojojin Najeriya sun samu nasarar cafke wasu mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane a garuruwan jihar Taraba. Wadanda ake zargin sun ba da bayanai.
Kasurgumin dan ta'adda, Bello Turji ya ce kafa shari'a da Ahmed Sani Yarima ya yi a Zamfara ce ta jawo aka fara cin mutuncin Fulani wanda hakan ya jawo ta'addanci.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun hallaka wani matashi bayan ya kai musu kudaden fansa a jihar Kaduna. 'Yan bindigan sun ce ya yi musu tsaurin ido ne.
Wau ‘yan bindiga da ake zargin mazauna Binuwai ne sun dira yankin Gugur da ke karamar hukumar Katsina-Ala tare da kashe mutane shida a harin ramuwar gayya.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari