Gwamnan Jihar Katsina
Maganganun da shugaban majalisar dattawa ya yi a kan gwamnonin jihohi ba gaskiya ba ne. Sanata Godswill Akpabio ya bada hakuri ta bakin mai magana da yawunsa.
'Yan bindiga sun kai hari kan wani masallaci a yankin Kankara yayin da ake sallar Isha'i inda suka hallaka mutane uku. Maharan sun kuma yi awon gaba da wasu da dama.
Gwamnan Katsina, Malam Dikko Radda, ya bayyana cewa Katsina na bukatar taimako domin samar da isasshen tsaro a makarantu domin dalibai su yi ilimi mai nagarta.
Mu na da labari Gwamnan Katsina Umar Dikko Radda ya bayyana cewar ’yan bindigar da jami’an tsaro suka hana sakat na farautarsa domin kawo masa hari.
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya sake jaddada matsayarsa cewa ya zama wajibi jama'a su tashi tsaye su kare kansu daga ƴan bindiga.
Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kura taron gaggawa kan tsadar rayuwa da kuma matsalar tsaron da ke neman dawowa a jiharsa ta Katsina.
Gwamnatin Katsina ta raba wa mata 18 da aka ceto N100,000 kowanen su bayan dakarun sojin Najeriya sun kutsa har cikin daji, sun yi gumurzu da ƴan bindiga.
Yan bindiga sun saki bidiyon 'yan mata 63, ciki har da wata amarya, kawayenta da 'yan uwanta da suka sace a karamar hukumar Sabuwa, jihar Katsina.
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radɗa ya tallafawa mutanen da sojoji suka kubutar daga hannun masu garkuwa da mutane domin su koma gida da ƙarfi.
Gwamnan Jihar Katsina
Samu kari