
Tsadar Mai







'Yan kasuwa dake cinikayya a kasuwanni da dama a Kano sun shaida wa Legit cewa akwai alamun saukin farashin kaya da ake samu a yanzu daga Allah ne kawai.

NMDPRA ta rufe gidajen mai 5 a Katsina saboda matse lita da rashin tsaro. NMDPRA ta zayyana sunayen gidajen da aka rufe suka hada da A A Rano, Ashafa da wasu uku.

Direbobin tankunan mai sun dakatar da ɗaukar kaya a Lagos, lamarin da ke barazana ga wadatuwar man fetur da dizal, tare da haddasa fargabar katsewar sadarwa.

Kungiyar direbobin manyan motoci ta bayyana cewa umarnin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayar a kan dakon mai zai rage shigo da fetur Arewa.

Kungiyar kasashe masu fitar da man fetur (OPEC) ta bayyana cewa Najeriya za ta iya rika fitar da gangar danyen mai akalla miliyan hudu a kullum saboda wasu dalilai.

Yayin da ake kokawa kan yawan haduran tankokin mai da ake samu, Hukumar NMDPRA ta haramta amfani da tankokin mai masu daukar lita 60,000 a hanyoyin Najeriya.

Matatar Dangote ta rage farashin dizal zuwa N1,020 daga N1,075, domin taimakawa masana’antu da ‘yan Najeriya wajen rage tsadar rayuwa da bunkasa tattalin arziki.

Gwamnatin jihar Neja ta bayyana cewa tallafin da Uwargidan Shugaban kasa, Oluremi Tinubu ta ba jihar zai karfafa wa jama'ar da gobara ta shafa gwiwa.

Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bayyana cewa ba a fahimce ta ba ne a kan kalamanta na kwanan nan da ke cewa za a kara kudin hasken wuta ga 'yan Najeriya.
Tsadar Mai
Samu kari