
Labaran kasashen waje







Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tashi zuwa birnin Paris, na kasar Faransa, a yau Laraba domin wata gajeriyar ziyarar aiki, kamar yadda fadar shugaban kasa ta sanar.

Masana falaki sun tabbatar cewa jinjirin watan Shawwal zai kasance a sararin samaniya, amma saboda matsalolin yanayi da warwatsewar haske, ba zai yiwu a gan shi ba.

Gwamnatin Birtaniya ta fitar da jerin kadarorin da wasu 'yan Najeriya 60 suka mutu suka bari, kuma har yanzu babu wani magajinsu da ya je ya karɓe su.

Shugaban Sudan ta Kudu, Salva Kiir, ya kama mataimakinsa, Riek Machar. Kasashen waje na rufe ofisoshinsu yayin da rikicin basasa ke shirin barkewa a kasar.

Shugabannin GAVI, kungiyar da ke bayar da tallafin rigakafi ka kasashe sun ce idan Amurka ta dakatar da tallafinsu, mutane miliyan 1.2 za su mutu a shekaru 5.

Jonathan ya lashe kyautar Sunhak Peace ta 2025. Tinubu ya taya shi murna, yana mai cewa karramawar ta tabbatar da rawar da yake takawa wajen samar da zaman lafiya.

Dakarun sojojin sudan sun kwace ikon mulki a fadar shugaban kasa bayan shafe shekaru ana yaki tsakaninsu da 'yan tawayen RSF. Mutanen kasar sun yi farin ciki.

Wata 'yar Najeriya, Funke Iyanda na fuskantar hukuncin daurin shekaru 10 a Amurka kan zargin zamba da karɓar $40,980 daga tallafin rashin aikin yi ba bisa ka’ida ba.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta ce ta kwashe fiye da shekara guda tana fama da yunkurin cin zarafi daga shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.
Labaran kasashen waje
Samu kari