Labaran kasashen waje
Makamai masu linzami daga Iran sun afka wa tsakiyar Isra'ila a ranar Laraba, inda suka jikkata mutane tara tare da janyo gobara a yankunan Bnei Brak da Petah Tikva.
Wani alƙalin babbar kotun tarayya ya dakatar da Shugaba Donald Trump daga ci gaba da gina katafaren zauren taro na dala miliyan 400 a fadar White House.
Rundunar IRGC ta Iran ta jero kamfanonin Amurka irin su Tesla da Google a matsayin halattattun wuraren kai hari idan aka ci gaba da kashe mata shugabanni.
Fadar shugaban kasar Faransa ta bayyana cewa kasar ba ta sauya matsayarta ba tun farkon yakin da Amurka/Isra'ila ta fara da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta sanar da samun amincewar ƙasashe 10, ciki har da Amurka da Birtaniya, kan naɗin sabbin jakadun da Shugaba Tinubu ya tura yau.
Farashin kowane galan na man fetur ya yi tashin gwauron zabo, ya haura Dala 4 a wasu jihohi a kasar Amurka, wannan ke karo na farko tun shekarar 2022.
Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian ya gode wa al'ummar kasar Iraki bisa kuna da goyon bayan da suke nuna masu a wannan lokaci da suke fuskantar yaki.
Dakarun sojojin Iran sun samu nasarar kakkabo jirgin leken asiri na MQ-9 da ke da alaka da kasashen Amurka da Isra'ila, an ce jirgin yana da matukar tsada.
Sanata Adam Schiff ya fito ya nuna adawarsa kan abin da ya kira yunkurin gwamnatin Amurka na rage kudin kiwon lafiyar jama'a domin samar da kudin yaki da kasar Iran.
Labaran kasashen waje
Samu kari