Yaki da cin hanci a Najeriya
Tsohon shugaban hukumar PCACC, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado ya kubuta daga hannun yan sanda bayan kama shi ranar Juma'a a ofishinsa da ke Kano.
Gwamnatin jihar Kano ta nuna damuwarta matuka kan yadda 'yan sanda suka cafke tsohon shugaban hukumar PCACC, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado jiya.
Jigon a APC a Kano, Alwan Hassan ya janye ikirarin cewa sanatoci sun karɓi dala miliyan 10 don jinkirta tantance Abdullahi Ramat a a matsayin shugaban hukumar NERC.
EFCC ta mayar wa wata tsohuwa mai shekara 70, Margret Taye Odofin, N42.5m da jami’ar banki ta sace mata, bayan shekara da dama tana neman adalci.
Rundunar ‘Yan sanda ta janye karar Naira miliyan 400 da ta shigar kan tsohon Sanata Andy Uba da abokinsa, bayan sulhu tsakanin ɓangarorin da ke rikici.
Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da sauran wadanda ake tuhuma a kotu sun kawo tsaiko a zaman ranar Litinin.
Hukumar EFCC ta tabbatar cewa tsohon Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, na nan ƙarƙashin bincike duk da komawarsa jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Gwamnatin Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje da ‘ya’yansa guda biyu da wasu kotu bisa zargin almundahanar N4.4bn kan aikin tsandauri a Dala.
EFCC ta gurfanar da tsohuwar shugabar NSITF, Ngozi Olejeme, kan tuhumar karkatar da N1bn da dala miliyan biyu; sai dai Ngozi ta ki amincewa da wannan tuhuma.
Yaki da cin hanci a Najeriya
Samu kari