Yaki da cin hanci a Najeriya
Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya kare kansa daga zargin ɓatan ₦128bn a hannun SERAP, yana jaddada cewa zargin ya faru kafin nadinsa a gwamnati.
Tsohon Antoni Janar kuma tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami (SAN) ya gurfana a gaban babbar kotun tarayya ta Abuja kan tuhumar karkatar da dukiyar kasa.
Gwamnatin tarayya ta shigar da tuhume-tuhume 16 na safarar kudi kan tsohon Ministan Shari’a a Najeriya, Abubakar Malami, bisa zargin boye kudaden haram.
Attajirin dan kasuwa a Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya yi wasu zarge-zarge game da badalakar cin hanci da rashawa da ya alakanta da hukumomin NMDPRA da NUPRC.
Tsohon shugaban EFCC, Ibrahim Magu, ya ce ba a gayyaci Goodluck Jonathan ba kan badakalar makaman saboda takardu sun nuna ba a amince da kudin don kamfen ba.
Hukumar yaki da cin hanci ta ICPC ta gayyaci Aliko Dangote domin bayar da ƙarin bayani kan ƙarar da ya shigar kan tsohon shugaban NMDPRA, Farouk Ahmed.
Gwamnatin Jihar Kebbi ta musanta zargin cewa tana da hannu a binciken da hukumar EFCC da ake yi wa tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami a Abuja.
Alwan Hassan, wani jigo a jam'iyyar APC ya ce Ministocin Buhari sun samu dama kuma sun yi yadda suka ga dama, ya ce galibinsu kamata ya yi a ce suna gidan yari.
Tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami ya ce tambayar da EFCC ta yi masa ta tsaya ne kawai kan batun zargin maimaita aikin dawo da kudin Sani Abacha.
Yaki da cin hanci a Najeriya
Samu kari