Yan bindiga
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Neja. 'Yan bindigan sun hallaka mutane da dama tare da yin garkuwa da wasu zuwa cikin daji.
Rahotanni sun nuna cewa harin sama da Amurka ta kai a daren Kirsimeti ya lalata sansanonin Lakurawa a dazukan Sokoto, inda ’yan ta’adda suka tsere.
Tsohon ɗan Majalisar Dokokin Jihar Ogun, Hon. Musa Moruf, ya samu ’yanci bayan kwana uku a hannun masu garkuwa da mutane bayan sace shi a masallaci.
Sanata mai wakiltar Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya yi tsokaci kan matsalar rashin tsaro. Ya ce ba Shugaba Bola Tinubu ba ne ke da alhakin samar da tsaro a jihohi.
'Yan bindiga sun kashe mutum 8 a ƙaramar hukumar Shanga, jihar Kebbi; ƴan sanda sun tabbatar da kisan mutane a Kaiwa da Gebbe yayin da aka fara farautar miyagun.
‘Yan bindiga sun kai hari inda suka sace Sarkin Aafin, Oba Simeon Olaonipekun, tare da ɗansa Olaolu bayan kai farmaki fadar sa a Ifelodun, Jihar Kwara.
Akalla mutum 9 ne aka kashe a wani sabon hari da aka kai ƙauyen Bum a Jos ta Kudu, jihar Plateau, a daren ranar Laraba, wanda ya shafi maza, mata da yara ƙanana.
Gwamnan Katsina, Dikko Radda, ya ce zaman lafiya na dawowa a wasu kananan hukumomi da ‘yan bindiga suka addaba, yana sa ran 2026 za ta fi armashi.
Rundunar 'yan sandan jihar Ondo ta tabbatar da harin da wasu 'yan bindiga suka kai wani ofishin 'yan sanda a jihar Ondo. Maharan sun kona ofishin kurmus.
Yan bindiga
Samu kari