
Zaben Shugaban kasan Najeriya







Jam'iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa maganar cewa akwai shirin sake tsayar da Goodluck Ebele Jonathan takarar shugaban kasa ba ta da tushe ballantana makama.

Rahotanni sun bayyana cewa akwai shirin da wasu 'yan siyasa ke yi na jawo tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan ya sake neman kujerar a zaben 2027 mai zuwa.

Tsohon sakataren yada labarai a PDP, Kola Ologbodinya ya bayyana fargaba a kan yiwuwar rugujewar jam'iyyarsa, wanda ya danganta da hukuncin da kotu za ta yanke masu.

Fitaccen malamin addinin Kirista a Najeriya, Fasto Chukwuemeka Cyril Ohanaemere ya bayyana kudurinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 mai zuwa.

Daya daga cikin jagororin PDP, Kola Ologhondinyan ya bayyana cewa APC ta kwana da sanin cewa akwai gagarumin shirin da zai kawo karshen mulkinta a 2027.

Ministan harkokin jiragen sama da ci gaban sashen, Festus Keyamo, ya bayyana cewa jam'iyyar PDP ba ta da katabus a zabe mai zuwa, wanda zai sa APC ta lashe zabe.

Tsohon Mataimakin Shugaban PDP na kasa, Bode George ya bayyana cewa PDP za ta yi babban kuksure matukar ta sake tsayar da Atiku Abubakar takarar shugaban kasa.

Sanata Orji Kalu ya bayyana cewa duk da Kudu maso Gabas na son samar da dhugaban ƙasa amma babu mai iya kayar shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Charles Udeogaranya ya ce littafin Babangida ya share hanya ga samar da shugaban ƙasa daga kabilar Ibo a 2027. Ya nemi APC, PDP su tsayar da dan yankin a zaben.
Zaben Shugaban kasan Najeriya
Samu kari