
Zaben Najeriya







Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa an samar da kawancen jam'iyyun adawa ne domin kawo karshen mulkin APC a kakar zaben 2027.

Tsohon Ministan yada labarai a gwamnatin Muhammadu Buhari, Lai Muhammad ya tabbatar da cewa sun nuna wa duniya cewa Bola Ahmed Tinubu ya ci zaben 2023.

Shugaban gwamnonin PDP, Bala Mohammed ya bayyana cewa suna yiwa tsohon dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar, Atiku Abubakar fatan alheri da hadakar jam'iyyunsa.

Dele Momodu ya ce kalubalantar Tinubu da Wike a 2027 tamkar gasar cin kofin duniya ce. Ya kuma soki gwamnonin PDP kan kin shiga kawancen hamayya.

Bayan gwamnonin PDP sun yi fatali da jita-jitar haɗaka, jigon jam'iyyar, Dele Momodu ya zarge su da kin hadin gwiwa da domin shirin marawa Bola Tinubu baya a 2027.

Fadar shugaban kasa ta hana fara yi wa Bola Tinubu da Kashim Shettima kamfen din zaben 2027. Bola Tinubu ya ce a gaba zai bayyana matsayarsa kan 2027.

Jagora a NNPP ya yi zargin cewa tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yi takaicin yadda Bola Ahmed Tinubu ya samu nasarar kama mulkin Najeriya.

Kungiyar dattawan Kudu maso Kudu ta bukaci 'yan Najeriya su zabi Bola Tinubu a 2027. Ta ce ya nada dan kabilar Ibo a limamin Abuja da ba su mukamai masu tsoka.

Shugaban hukumar INEC, Mahmood Yakubu ya bayar da tabbacin cewa wa'adinsa a matsayin shugaban hukumar zaben ya zo karshe, kuma zai ajiye aiki a karshen shekara.
Zaben Najeriya
Samu kari