
Jihar Edo







Babban limamin Edo, Sheikh Abdulfattah Enabulele ya nuna rashin amincewarsa kan matakin kulle makarantu da wasu gwamnonin Arewa suka dauka saboda azumin Ramadan.

Gwamnatin jihar Edo ta gano wasu gidaje da masu garkuwa da mutane suke boye wadanda suka sace a cikin gari. An rusa gidajen tare da gargadin al'umma.

Rundunar ƴan sanda ta samu nasarar kama mutum 4 da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki cocin Katolika a jihar Edo, maharan sun yi garkuwa da limami da ɗalibi.

Wani ango, Kelvin Izekor ya kashe matarsa mai suna Success a Edo, bayan ya sare ta da adda. ’Yan sanda sun cafke shi shi, kuma yanzu yana gidan yari ana bincike.

Tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Edo a inuwar jam'iyyar LP, Olumide zakpata ya sanar da rasuwar mahifinsa da kuma kawunsa, ya ce rashinsu ya jijjiga shi.

Rikicin kabilanci tsakanin mazauna garuruwan Gbelemonti da Maidoti a jihar Edo ya jawo mutuwar mutane 7, tare da jikkata 6. ‘Yan sanda da sojoji sun dakile lamarin.

Gwamna Monday Okpebholo ya bayyana cewa babu wani ubangidanda da yake juya shi yadda yake so, ya ce waɗanda ake alaƙanta da shi su taimakonsa suka yi.

Hedikwatar Raabitatul Aima Wal Hulamoh ( kungiyar limamai da malamai) na yankin Yarbawa ta sanar da ranar fara azumin watan Ramadana na 2025 a Najeriya.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an gano mawaki, Innocent Idibia da masoyiyarsa yar majalisar Edo, Natasha Osawaru duk da gargadin mahaifiyarsa kan lamarin.
Jihar Edo
Samu kari