
Zaben Edo







Dan takarar gwamnan Edo a zaben 2024, Asue Ighodalo ya maka shugaban jam'iyyar APC na jihar, Jarret Tenebe, a kotu kan zargin bata suna. Ya na neman diyyar N500m.

Jam'iyyar APC ta kwato babban ofishinta da PDP ta kwace tsawon shekaru hudu a jihar Edo. Shugaban APC ya ce za su cigaba da tsare kadarorin jam'iyyar.

Jam'iyyun PDP da APC sun harbi juna da maganganu bayan an kai hari ana tsaka da zaman kotun sauraron karar gwamnan jihar Edo. APC da PDP sun zargi juna.

Da safiyar Laraba bayan fara zaman kotun sauraron kararrakin zaben gwamna a Edo, an jiyo karar harbe-harben bindiga, lamarin da ya tada hankulan lauyoyi da alkalai.

Shugabar ƙaramar hukumar Egor s jihar Edo ta yi watsi da matakin wasu kansiloli na sauke ta daga kan kujerar mulki, ta ce hakan ya saɓawa kundin tsarin mulki.

Gwamnan Edo ya rantsar da shugabannin riko duk da hukuncin kotu, yayin da Antoni Janar ya jaddada cewa dakatarwa na shugabannin iko ne na kansiloli kawai.

Babbar kotun jihar Edo mai zama a Benin City ta maido da ciyamomi da mataiamkansu da majalisa ta dakatar, ta ce a bari sai ta yanke hukunci kan karar da ake gabanta.

Bayan kai ruwa rana a zaman ranar Talata, Majalisar dokokin jihar Edo ta dakatar da shugabanni da mataimakansu a kananan hukumomi 18 na jihar kan zargi.

Sanata Monday Okpebholo ya rusa dukkan hukumomin da ke karƙashin gwamnatin jihar Edo, ya umarci shugabanni da mambobi su miƙa kayan da je hannunsu.
Zaben Edo
Samu kari