Matsin tattalin arziki
Jam'iyyar adawa ta ADC ta ce gwamnatin tarayya karkashin Bola Tinubu ta siyasantar da fama da wahaalar abinci da ake a Najeriya. Bolaji Abdullahi ne ya fadi haka.
Farashin shinkafa ya fadi sosai a kasuwannin Lagos saboda karin shigo da ita ta iyakoki, lamarin da ya rage wa masu saye ciniki wanda ya jawo faduwarta.
Fadar shugaban kasa ta fitar da farashin kayan abinci a Najeriya. Ta ce farashin shinkafa, masara, wake, manja da sauran kayan masarufi sun sauka a kasuwannin kasa.
Gwamnatin Jihar Lagos ta rushe kasuwar Costain da ke jihar, inda ta kori ‘yan kasuwa da dama tare da lalata kadarori masu darajar miliyoyin naira.
Farashin gas ɗin girki ya sauka daga N2,000 zuwa N1,300/kg, yayin da gwamnati ke sa ido kan masu boye kaya da dillalai don ganin farashin ya daidaita a kasuwa.
Atiku Abubakar ya bayyana damuwa kan yadda talauci ke karuwa a Najeriya duk da albarkatun kasar. Ya bukaci gwamnati da kungiyoyi su hada kai wajen yaki da talauci.
Bankin Duniya ya ce yawan jama’ar Najeriya na iya ƙaruwa da mutum miliyan 130 nan da 2050, abin da zai iya zama barazana ko dama ga ci gaban mutane.
Rauf Aregbesola ya zargi APC da jawo yunwa, talauci da rashin tsaro a Najeriya, yana mai cewa ADC ce zabin jama'a wadda za ta cika alkawuranta a 2027.
Jam'iyyar 'yan adawa ta ADC ta bayyana damuwa a kan yadda APC ta ke tattare manyan 'yan siyasar kasar nan zuwa cikinta, sai dai ta ce hakan ba zai dakile ta ba.
Matsin tattalin arziki
Samu kari