Arewa
Tsohon ɗan takarar gwamna a jam'iyyar SDP a jihar Kogi, Muritala Ajaka, ya yi alhininsa kan rasuwar Sarkin Elaite yana cewa marigayin mutum ne mai son zaman lafiya.
Majalisar dokokin jihar Adamawa ta bai wa gwamna karfin iko mada mai rikon lwarya idan sarki KO hakimi na kwance yana fama da rashin lafiya ko ya gaza aiki.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya taya Etsu Nupe, Alhaji Yahaya Abubakar murna bisa cika shekara 73 da kuma zagayowar shekaru 22 a karagar mulki.
Tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami ya zargi gwamnan Kebbi da shirin shigo da yan daba, sojojin haya don danne yan adawa, ya zarge shi da alaka da Lakurawa.
Ana fargabar cewa za a samu ambaliyar ruwa a jihohin Legas, Ogun, Akwa Ibom, da Cross River a ranar Juma'a, 12 ga Satumba, 2025. NiMet ta ce za a sha ruwa a Arewa.
Gwamnatin Kebbi karkashin Gwamna Nasir Idris, ta dakatar da kwamishinan lafiya na jihar, Yunusa Isma’il. An bukaci ya kare kansa ko ya fuskanci wani hukuncin.
A karon farko a tarihi mace ta shiga an yi hawan sallar gani da ita a Daura jihar Katsina, Sarauniyar kasar Hausa, Dr. Lubna Mohammed Gusau ce ta kafa tarihin.
Sojojin Operation Fansan Yamma da jami’an tsaro sun yi nasarar dakile yunkurin ‘yan bindiga na kai hari wani kauyen karamar hukumar Malumfashi, an rasa rayuka.
Jihohi 31 sun tara wa kansu bashin N2.57tr amma ba su iya jawo jarin waje a zangon farko na 2025 ba; jihohi 10 kadai sun karbo bashin N417bn duk da karin FAAC.
Arewa
Samu kari