Aikin Hajji
Mai shari’a K.B. Olawoyin na babbar kotun Oyo ya haramtawa Sarkin Ogbomoso, Oba Afolabi Ghandi Olaoye tsige babban limamin Ogbomoso, Sheik Teliat Yunus Ayilara.
Sarkin Ogbomoso da ke jihar Oyo, Oba Afolabi Ghandi ya kalubalanci limamin masallacin Juma'a kan saba ka'idar da suka yi kafin nada shi mukami a jihar.
Hukumomi a kasar Saudiyya sun sanar da rasuwar wasu mahajjatan Najeriya da dama yayin aikin hajjin bana na shekarar 2024 da muke ciki daga jihohi daban-daban.
Hukumar NAHCON ta jinjinawa mahajjaci mai suna Muhammad Na'Allah daga yankin Gummi a jihar Zamfara da ya mayar da kudin tsintuwa da suka kai €1,750.
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya bukaci majalisar tarayya da ta binciki tallafin N90bn da gwamnatin tarayya ta ba hukumar NAHCON domin hajjin bana.
Kungiyar 'yan jarida ta IHR ta jinjinawa hukumar jin dadin alhazai a jihar Kaduna bayan dawowa mahajjata kudi kimanin $50 saboda sauki da aka samu kan hadaya.
Jirgin farko da ya kwaso alhazan Najeriya daga Saudiya ya Iso gida. Kashi na farko na alhazai 410 daga jihar Kebbi da suka yi aikin Hajjin bana sun dawo gida.
Mai gadi da ke rike da makullin Ka'abah, Dakta Saleh Bin Zain Al-Shaibi ya rasu da safiyar yau Asabar inda aka yi sallar jana'izarsa a Masallacin Harami.
Rahotanni sun bayyana cewa Ƙasar Masar ta rasa alhazai 600 waɗanda suka rasu sakamakon tsananin zafin da aka yi fama da shi a aikin hajjin bana a Saudiyya.
Aikin Hajji
Samu kari