Abun Bakin Ciki
Mazauna Borgu da Agwara a jihar Niger na tserewa gidajensu bayan kisan mutane fiye da 40; sun koka kan janyewar sojoji yayin da ’yan bindiga ke yi musu barazana.
Gwamnan jihar Bayelsa, Douye Diri ya yi alhinin rasuwar tsohon sanatam jihar, Brambaifa, wanda Allah ya yi wa rasuwa a wani asibiti a birnin tarayya Abuja.
Iyalai sun tabbatar da cewa gawar sanatan Nasarawa ta Arewa, Godiya Akwashiki ta iso Najeriya, kuma ana ci gaba da shirye-shiryen yi masa sutura a Abuja.
An binne tsohon Kwamishinan Ilimi na jihar Kaduna, Alhaji Suleiman Lawal Kauru, a Zaria bayan ya rasu yana da shekaru 78 a asibitin koyarwa na ABUTH da ke Shika.
Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan mutum 30 a kasuwar jihar Niger, tare da jajantawa jihar Yobe kan haɗarin jirgin ruwa da ya kashe mutane 25.
Gobara ta lalata ofisoshi da taskar makamai ta rundunar ‘yan sandan Mopol 13 a Makurdi, jihar Benue; rundunar ta tabbatar da faruwar lamarin tare da fara bincike.
Mutum 25 sun rasu, 14 sun ɓace a haɗarin jirgin ruwa a Nguru, Yobe; Hukumar SEMA ta ceto mutum 13 yayin da ake ci gaba da neman waɗanda suka ɓace.
Cocin Katolika na Issele-Uku a Jihar Delta ya tabbatar da rasuwar Limami kuma Fasto Stephen Chukwuma, wanda ya rasu a daren sabuwar shekara yayin huduba.
Za a yi jana’izar abokan Anthony Joshua biyu da suka rasu bayan hatsarin mota a Najeriya, an shirya sallar a Masallacin London ranar Lahadi, 4 ga Janairu 2026.
Abun Bakin Ciki
Samu kari