Abuja
Kotun tarayya ta ba da belin Farfesa Usman Yusuf bayan gurfanar da shi da hukumar EFCC ta yi. EFCC ta zargi tsohon shugaban NHIS da almundahanar kudi.
Kamfanin MRS ya rage farashin man fetur a dukkan gidajen mansa a Najeriya. MRS ya sauke farashi ne bayan matatar Dangote ta rage kudin man fetur.
Bayan ce-ce-ku-ce kan rashin halartar Nasir El-Rufai taron APC, jam'iyyar ta yi wa tsohon gwamnan Kaduna martani kan kalamansa game da dalilin kin zuwa taron.
Bayan ce-ce-ku-ce kan rashin halartar Nasir El-Rufai da Muhammadu Buhari taron APC, tsohon gwamnan Kaduna ya fadi dalilin rashin halartar taron jam'iyyar da aka yi.
Jiga-jigan APC, da suka hada da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa'i ba su halarci babban taron jam'iyyar ba.
Rundunar 'yan sanda ta tabbatar da cewa 'yan bindiga sun kai hari kusa da barikin soji na Sani Abacha a birnin tarayya Abuja. Sun sace mutane sun motocinsu.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi magana kan tallafin man fetur a taron APC a Abuja. Bola Tinubu ya ce tsaro na inganta kuma tattali na kara habaka a Najeriya.
An shirya gudanar da NEC na APC yau a Abuja. Ganduje ne ke jagoranta, yayin da ake sa ran Tinubu zai yi jawabi kan ci gaban jam’iyya da shirin mulkinsa.
Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci (NSCIA) karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar ta bukaci Majalisar Dattawa ta cire wasu sassan kudirin haraji.
Abuja
Samu kari